Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ya ruwaito cewa, domin tunawa da ranar shahadar babban bawan Allah, Imam Zainul Abidin (A.S), an gabatar da jawabi wajen bayyana sassan "Sahifatus Zuhd" na wannan gagarumin Imami; littafin da yake nuna takawa ta basira, tauhidi, da tsayin daka wajen fuskantar azzalumai a makarantar Imam Sajjad (A.S). A wannan zama, Hujjatul Islam Wal Muslimin Muhammad Ali Murawwaji Tabasi, mamba a tsangayar ilimi ta Jami'ar Hazrat Masuma (SA), ya binciko bangarorin siyasa da na ibada na rayuwar Imami na Hudu.
Bismillahir Rahmanir Rahim
Yayin da nake mika ta'aziyyar shahadar ban tausayi ta Aba Abdillahil Husain (A.S), 'ya'yansa da sahabbansa masu aminci; bisa ga wata ruwaya, yau (12 ga Muharram) ita ce ranar shahadar jagora na hudu na mabiya tafarkin Ahlul Baiti wato Hazrat Imam Zainul Abidin, Ali bin Al-Husain (A.S).
Ci gaba da Tafarkin Wilayah a Mafi Wahalar Lokaci a Tarihi; Matsayin Imam Sajjad (AS) Wajen Tarbiyantar da Rukunonin Muminai Masu Juriya
Gaskiyar magana ita ce, yin magana game da Imam Sajjad (A.S) yana da wahala kamar yadda girman lamarin Karbala yake; Mutum zai iya magana kan girman halayensa ne kawai idan zai iya bayyana ainihin hakikanin abin da ya faru a dandalin Karbala. Kafin in bayyana maganganuna, zan kawo wasu jumloli daga Jagoran Juyin Juya Hali game da wannan mutum mai girma.
Jagora yayin da yake siffanta sirar Imami na Hudu yana cewa: "Ainihin fuskar Imam Sajjad (A.S) ita ce fuskar gwarzon mayaki, marar kasala, wanda ba ya tattaunawa da makiya, kuma mai haske wanda da cikakken tsari da kyakkyawan hangen nesa yake gano hanyoyi, yake zaba kuma yake mikawa zuwa ga manufa; Shi ba ya kasala, kuma yana gajiyar da makiyi." (Bayanin Jagora a watan Muharram na shekarar 1365)
Gina Kwararru da Sake Fasalin Al'umma a Lokacin Mulkin Kama-Karya na Bani Umayya
Jagora ya bayyana cewa, a cikin daukacin rayuwar shekaru dari biyu da hamsin na kaddamar da rayuwar A'imma (A.S), babu wani lokaci da ya kasance mai daci, wahala da jarrabawa kamar shekarun farko na imamancin Imam Sajjad (A.S). Lallai, ni da ku malamai da masana da kuka koya a karkashin minbarorin Husaini, mun tabbatar da cewa Imam na Hudu ya dauki nauyi mai nauyi na masifu a farkon shekarun imamancinsa.
Imam Zainul Abidin (A.S) ya yi imamanci na tsawon shekaru talatin da biyar. Shi, bisa hikima da maslahar Ubangiji don kiyaye hanyar sadarwa ta imamanci, ya fuskanci rashin lafiya mai tsanani a wani lokaci. Wannan bawan Allah ya rayu a lokaci mai matukar wahala, cike da kunci da bakin ciki; Saboda haka, magana kan girmansa yana da matukar wahala.
Imam Sajjad (A.S) ya rayu a lokacin zalunci da matsin lamba na la'ananniyar gwamnatin Bani Umayya; Gwamnatin da ta zarce dukkan masu laifi na tarihi. Bayan faruwar lamarin Karbala, ya kasance yana zaune a Madina, kuma daya daga cikin muhimman ayyukansa, kamar yaddda Jagora ya fada, shi ne gina kwararru. Ya yi hakan ne da manufar sake gina al'umma, tarbiyantar da kwararrun muminai, da shirya mutane don kafa gwamnatin Allah a karkashin jagorancin Ahlul Baiti (A.S).
Matsayin Shiryarwar Imam Sajjad (AS) wajen Farkar da Ruhin Al'umma
Daya daga cikin ayyukan Imam a wannan fanni shi ne yi wa mutane wa'azi da suka dace da yanayin lokacin. A cikin ruwayoyi an bayyana cewa, shi a kowace ranar Juma'a a Masallacin Manzon Allah (S.A.W.A) yana yi wa mutane wa'azi, yana kwadaitar da su zuwa ga lahira, sannan yana yi musu gargaɗi game da son duniya. Marigayi Kulaini a cikin littafinsa mai daraja na "Kafi" ya ruwaito da ingantaccen sanadi daga Abu Hamza Al-Thumali cewa: "Ban taba ganin wani wanda ya fi Ali bin Al-Husain (A.S) gudun duniya ba, in ban da abin da na ji game da Ali bin Abi Talib (A.S)." Abu Hamza ya ce majalisar wa'azi ta Imam ta kasance tana taba zukatan kowa da kowa.
A wannan taro mai haske, za mu kawo tare da yin bayani kan wani ingantaccen hadisi daga gare shi a wannan fanni.
Ma'anar Ɗagutu da Alakar Gudun Duniya da Basirar Siyasa
Abu Hamza Al-Thumali ya ruwaito cewa: "Na sami wani rubutu da yake dauke da kalaman Imam Sajjad (A.S) game da zuhudu (gudun duniya); na kai shi ga Imam, kuma bayan ya karanta, ya tabbatar da ingancin rubutun."
Wannan rubutu da aka sani da "Sahifatus Zuhd", yana nuna cewa Imam Zainul Abidin (A.S) ya bayyana wadannan kalamai ne a gaban wasu kebantattun mutane; mabiya wadanda suka yi amanna da wilayah ta Ahlul Baiti (A.S) kuma suke kallon gwamnatin Bani Umayya a matsayin "Ɗagutu" da kuma gwamnatin da ba halastacciya ba. A nan gaba za mu kawo wasu sassa na wannan haskakan kalamia.
Wadannan bayanai sun fara da wadannan jumloli:
«بسمالله الرحمن الرحیم؛ کفانا الله و إیاکم کید الظالمین و بَغی الحاسدین و بطش الجبارین. أیها المؤمنون، لا یفتننّکم الطواغیت و أتباعهم من أهل الرغبة فی هذه الدنیا، المائلون إلیها، المفتونون بها، المقبلون علیها...»
Imam yana cewa yayin da yake jawabi ga wannan kungiya ta mutane na musamman mabiya Ahlul Baiti (A.S): "Allah ya tsare mu da ku daga makircin azzalumai, fin karfin masu hassada, da farmakin masu girman kai. Ya ku muminai! Kada ku bari dagutai da mabiyansu masu son duniya su rude ku, su jefa ku cikin fitina."
Daya daga cikin muhimman bangare a wannan sashi shi ne yadda Imam (A.S) ya siffanta gwamnatin azzalumai da sunan "Dawagit" (Dagutai). "Dagut" kalma ce ta Alkur'ani da take nufin mai tsaurin kai da ketare iyaka, kuma ana amfani da ita ga kowane mutum ko gungun mutane da suka tayar da kayar baya ga umurnin Allah kuma ake yi musu biyayya a maimakon gaskiya; Walau shaidan ne, gumaka ne, ko kuma sarakuna masu kama-karya da suka kwace hakkin shugabanci na Ahlul Baiti (A.S).
Dukkan wadanda suka tsaya a matsayin azzalumai kuma masu ketare iyaka, shugabannin bata wadanda suka batar da kansu kuma suka batar da wasu, muddin ana yi musu biyayya, to ana kiran su "Dagut". Allah Madaukakin Sarki ya ambaci kalmar Dagut sau da yawa a cikin Alkur'ani mai girma inda yake cewa:
«وَٱلَّذِینَ ٱجۡتَنَبُواْ ٱلطَّـٰغُوتَ أَن یَعۡبُدُوهَا وَأَنَابُوٓاْ إِلَی ٱللَّه لَهُمُ ٱلۡبُشۡرَیٰۚ فَبَشِّرۡ عِبَادِ»
Nisantar dagutu, musanta shi da yaki da shi, sune sharadin samun tauhidi da kadaita Allah.
Mutum yana bukatar ko dai ya bauta wa Allah ko kuma ya bauta wa Fir'auna; Ko dai ya yi biyayya ga Ubangiji ko kuma ya yi biyayya ga sarakunan Bani Umayya da shugabannin kafirai. A yau ma, gwamnatin Amurka da ta Isra'ila sune manyan misalan tsarin dagutu, kamar yadda kafin juyin juya hali, tsarin mulkin Pahlavi ya kasance cikakken misali na dagutu. Idan muna son zama masu kadaita Allah na gaskiya, dole ne mu yi watsi da Ɗagutu kuma mu musanta shi. Kasashen yankin su ma za su iya shiga da'irar tauhidi ne kawai idan suka 'yanta kansu daga mamaya da biyayya ga tsarin kafirci.
Abin sha'awa a wa'azin Imam Sajjad (A.S) shi ne cewa ba ya daukar "Zuhudu" (gudun duniya) a matsayin nuna halin ko-in-kula ga al'amuran siyasa. Bisa ga abin da yake cikin "Sahifatus Zuhd", sharadin zama mai tsoron Allah shi ne sanin makiya da gano dagutun zamani. Imam (A.S) yana yi wa mabiyansa gargadi game da yaudarar fuskantar fitinar dagutu. Asalin Musulunci a tsarinmu shi ma ya ginu ne a kan wannan harsashi; Kamar yadda tutarmu take dauke da sunan Allah mai tsarki da kuma kalmar "La ilaha illallah" wadda ba ta da wata ma'ana face kore Ɗagutu da tabbatar da bauta ga Allah.
Domin isa ga hakikanin "Allah" da tabbatar da tauhidi, babu mafita face kore "La ilaha"; wannan shi ne ginshiki na asali da dole ne a kiyaye shi a cikin lissafinmu da mahangarmu ta duniya.
Darussan Tarihi da Tsayin Daka a Tafarkin Sarautar Allah
Imam Zainul Abidin (A.S) a wani sashi na "Sahifatus Zuhd" ya yi rantsuwa sannan ya fuskanci mutanen zamaninsa yana cewa: "Na rantse da raina, ku kalli tsohon tarihinku ku gani me azzaluman sarakuna suka yi muku." Wannan gargaɗi yana duba ne ga jerin laifuffukan Banu Umayya wadanda suka fara tun lokacin Mu'awuya da kisan gilla ga sahabbai kamar "Hujr bin Adi" kuma ya kai kololuwa a zamanin Yazid.
Faruwar lamarin Karbala da laifukan Banu Umayya a wannan rabin yini na tarihi, inda ba su ji tausayin yara ba, kuma ba su girmama mata ba, bangare guda ne kawai na wannan bakin labari. Waƙi'ar "Harrah" wata shaida ce ta daban; inda mutanen Yazid suka halatta jini, rai, da dukiyar mutanen Madina na tsawon kwanaki uku, kuma suka kashe dubban mutane, ciki har da mahaddata Alkur'ani da sahabban Manzon Allah (S.A.W.A).
Imam Sajjad (A.S) ta hanyar tunatar da wadannan fitintinu da hargitsi na baya, ya jaddada cewa dole ne a yi amfani da darussan tarihi domin nisantar batattu, masu bidi'a, da masu barna a bayan kasa. Ya tambaya cewa wadannan gwamnatoci na zalunci, in ban da tauye tsaro da jin dadin rayuwa, wane abu ne mai kyau suka kawo wa mutane?
Wannan koke da tunatarwa ta Imami na Hudu tana ci gaba da amsa kuwwa a kunnuwanmu a yau. Idan muka kalli zamaninmu na yanzu, a cikin shekaru takwas na yakin da aka kakabawa Iran, wanene bai sani ba cewa Amurka da Isra'ila yar mamaya sune masu marawa jam'iyyar Ba'ath baya ba?
Yakinmu na yau da tsarin mulkin mallaka da girman kai yana da tushe na Alkur'ani: «وَالَّذِینَ اجْتَنَبُوا الطَّاغُوتَ». Hakikanin tauhidi da kadaita Allah yana cikin korewa da musanta Ɗagutu da bauta wa Allah makadaici kawai.
Bayan haka, Imam Zainul Abidin (A.S) ya bayyana hanyar tsira inda yake cewa:
«وَاستَعینوا بِاللَّه... وَ ارجِعوا إلی طاعَةِ اللَّه»
"Ku nemi taimako a wurin Allah... kuma ku koma ga biyayyar Allah da biyayyar wadanda suka cancanci a bi su.
Shi (Imam) a wani sashi daban, ya jaddada komawa ga tafarkin "Ulil Amr". Bisa ga aya mai girma:
«أَطیعُوا اللَّهَ وَ أَطیعُوا الرَّسُولَ وَ أُولِی الْأَمْرِ مِنْکُمْ»
Ulil Amr bayan Annabi mai tsarki (S.A.W.A), sune Amirul Muminina (A.S) da magadansa tsarkaka daga Ahlul Baiti.
Fiye da darare dari da Allah Madaukakin Sarki ya ba mu damar kasancewa a dandalin gwagwarmaya kuma muka rike tutoci a kan tituna, duka wadannan sun kasance ne domin kafa addinin Allah, tabbatar da wilaya ta Allah, da kafa makarantar Ahlul Baiti (A.S). Ku duba yadda Imam Sajjad (A.S) har a wancan lokacin na zalunci da kama-karya, bai daina gina kwararru da tarbiyantar da dakarunsa ba.
Babban darasi daga gare shi shi ne cewa bai kamata a gajiya da yaki ba; Yaki da dagutu zai ci gaba har sai bayyanar mai ceton duniya, Hazrat Waliyyul Asr (A.F). Mu muna da alhakin rike tutar yaki da kafirci da dagutun zamaninmu cikin juriya. Babu shakka wannan tafarki yana tafiya ne da "raunin zuciya" da wahalhalu masu yawa, amma karshensa shi ne cewa da yardar Allah yayin juyin juya hali na duniya na Hazrat, za mu mika wannan tutar zuwa ga hannunsa mai albarka cikin fara'a da mutunci.
Ra'ayinka